Sabon kawance na yan adawa a Nijar
A Jamhuriyar Nijar, tsohon Ministan harakokin wajen kasar Ibrahim Yakouba da shugaban Nijar Mahamadou Issifou ya salama a watan Afrilu ya kafa sabuwar kawance ta biyar da ta hada jam’iyyoyin adawa, kungiyoyin farraren hula da aka yiwa sunan Front Patriotique domin kare demokkuradiya a kasar ta Nijar.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
An dai gudanar da wannan gaggarumin taro a dakin taro na palais de Congres na birnin Yameh,inda Ibrahim Yakouba shugaban wannan gungun ya bayyana cewa gwamnatin Mahamadou Issifou ba ta cika alkawura da ta dau a baya ba, sai dai wani abin lura shine ga baki dayan su manyan yan siyasa bangaren adawa ba su halarci wannan zaman taro ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu