Isa ga babban shafi
Mali

Yan adawa sun gudanar da zanga-zanga a Bamako

Yan adawa sun fito a jiya juma’a a babban birnin Bamako na kasar Mali domin tilasatawa Gwamnatin kasar daukar alkawali na shirya sahihin zaben shugaban kasa na ranar 29 ga watan yulin shekarar nan da muke ciki.

Masu zanga-zangar lumana a Jamhuriyar Mali
Masu zanga-zangar lumana a Jamhuriyar Mali Michele CATTANI / AFP
Talla

Domin kaucewa sake fuskantar tashin hankali hukumomi a Bamako sun aike da jami’an tsaro da suka tabbatar da tsaro a lokacin wannan zanga-zanga.

Yan adawan dauke da sakonni inda ake iya karanta cewa sahihi zabe demokuradiyya kenan, sun bukaci Shugaban kasar Ibrahim Bubacar Keita da ya nisan ta kan sa daga abinda yan adawa ke kira kokarin kawo cikas ga demokuradiyyar kasar Mali.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.