Bakonmu a Yau
Bashir Ladan kan bukatun da 'yan awaren kasar Kamaru suka mika wa gwamnati
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:36
Masu fafutukar ‘yantar da yankin Kamaru dake amfani da harshen Ingilishi, sun bukaci gwamnatin kasar ta soke dokar yaki da ta’addanci da yi wa magoya bayan su afuwa a wani yunkurin sasanta rikicin yankin.Cikin wasu bukatu da suka gabatarwa kwamitin sasanta rikicin da ake samu, masu fafutukar sun bukaci gwamnati ta bayar da damar mayar da gawar tsohon shugaban kasa Amadou Ahidjo gida.Dangane da wadanna bukatu Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Bashir Ladan, Dan Jarida a kasar Kamaru kuma ga yadda zantawar su ta gudana.