Isa ga babban shafi
Lafiya

Mutane 5 sun sake kamuwa da cutar Ebola a Jamhuriyar Congo

Ma’aikatar lafiya ta Jamhuriyar Congo sun sanar da gano wasu karin mutane 5 da suka kamu da cutar Ebola, a yankin arewa maso yammacin kasar.

Wasu jami'an lafiya da ke lura da masu fama da cutar Ebola a Jamhuriyar Congo.
Wasu jami'an lafiya da ke lura da masu fama da cutar Ebola a Jamhuriyar Congo. AFP Photo/Junior D. Kannah
Talla

Uku daga cikin mutanen mazauna kauyen Bikoro ne, inda cutar ta fara sake bulla a makwannin baya, yayinda sauran biyun da suka kamu ke Wangata.

Sabon al’amarin yazo ne a dai dai lokacin da hadin gwiwar gwamnatin jamhuriyar Congo da hukumar lafiya ta duniya WHO ke kokarin shawo kan cutar da ta sake barkewa a makwannin baya, inda zuwa yanzu sama da mutane 50 suka sake kamuwa da ita, wasu 25 kuma suka mutu a dalilin cutar.

Ranar 8 ga watan Mayu da ya wuce, ma’aikatar lafiya ta Jamhuriyar Congo, ta tabbatar da sake bullar cutar Ebola a kauyen Bikoro da ke arewa maso yammacin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.