Isa ga babban shafi
Libya

Masu safarar mutane sun hallaka bakin-haure a Libya

Majalisar Dinkin Duniya ta ce masu safarar mutane a Libya sun harbe wasu bakin- haure 12 har lahira, tare da jikkata wasu da dama, yayinda suka yi kokarin tsrewa daga sansanin da suka tsare su.

Wasu daga cikin bakini-haure 'yan nahiyar Afrika da aka tsare a wasu sansanoni da ke babban birnin kasar Libya Tripoli.
Wasu daga cikin bakini-haure 'yan nahiyar Afrika da aka tsare a wasu sansanoni da ke babban birnin kasar Libya Tripoli. Reuters
Talla

Lamarin wanda ya auku a garin Bani walid da ke kudu maso gabashin Tripoli ya faru ne tun a ranar 23 ga watan Mayun da ya gabata, amma sai a baya bayan nan majalisar dinkin duniyar ta bayyana aukuwarsa.

Majalisar ta ce sansanin da bakin-hauren sukai yunkunrin tserwa ya kunshi ‘yan kasashen Eritrea, habasha da kuma Somalia, wadanda yawansu ya haura 200

Bincike ya nuna cewa gungun masu safarar mutane sun tafiyar da sansanoni akalla 20, wadanda cikinsu suke tsare da bakin-haure da ke fafutukar tafiya zuwa turai ko ta wane hali a garin na Bani Walid da ke kasar ta Libya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.