Isa ga babban shafi
Jamhuriyar demokradiyyar Congo

An fara yiwa jama'a rigakafin Ebola a Jamguriyar Congo

Jami’an lafiya Jamhuriyar Congo sun fara aikin baiwa jama’a rigakafin cutar Ebola, a yunkurin da ake na dakile sake bazuwar cutar zuwa sassan kasar. Cutar Ebolar dai na ci gaba da yaduwa a kasar duk da matakan da hukumomin ke dauka na ganin sun dakile ta.

Wannan dai ba shi ne karon farko da Jamhuriyyar Dimokradiyyar Congon ke fuskantar annobar cutar ta Ebola ba.
Wannan dai ba shi ne karon farko da Jamhuriyyar Dimokradiyyar Congon ke fuskantar annobar cutar ta Ebola ba. REUTERS/Tommy Trenchard
Talla

An dai taba amfani da maganin rigakafin a tsakanin shekarun 2014-2016, kuma an samu nasara a wancan lokacin.

Faran aikin rigakafin ya zo a dai dai lokacin da ma’aikatar lafiyar kasar ta sanar da karuwar wadanda suka hallaka a dalilin kamuwa da cutar zuwa 26 bayan mutuwar wata jami’ar jiyya.

Tuni dai kasashen Nahiyar Afrika suka fara daura damarar ganin sun kare al'ummarsu daga cutar ta Ebola mai hadarin gaske.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.