Isa ga babban shafi
Cote D'Ivoire

Ana ci gaba da rage yawan sojoji a Cote D'Ivoire

Gwamnatin Cote d’ivoire na cigaba da rage yawan sojojin kasar domin rage adadin kudaden da kasar ke kashewa ta bangaren tsaro.

Dakarun kasar Cote d'ivoire a birnin Abidjan
Dakarun kasar Cote d'ivoire a birnin Abidjan SIA KAMBOU / AFP
Talla

Kakakin gwamnatin kasar Bruno Kone, ya ce yanzu haka akwai wasu jami’an tsaro 2.168 da suka amince a sallame su daga aiki karkashin wannan shiri da gwamnatin ke kan aiwatarwa.

A jimilce dai kasar Cote D’Ivoire na da dakarun da yawansu ya kai dubu 25 cikin har da tsoffin ‘yan tawaye.

Matakin zai taimaka sosai wajen rage yawan kudaden da gwamnatin kasar ke kashewa a duk shekara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.