Isa ga babban shafi
Najeriya

Jahilci ne ya haddasa rikicin Makiyaya da Manoma - Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce idan da bai yi karatu ba shima da ya kasance cikin rikicin Makiyaya da Manoma da ya addabi kasar tare da gurgunta al'amuran tsaro a wasu yankunan.

A cewar Muhammadu Buhari idan da ace bai yi karatu ba, da wata kila shi ma ya tsinci kansa a rikicin Makiyaya da Manoma da ke barazana ga harkokin tsaron Najeriyar.
A cewar Muhammadu Buhari idan da ace bai yi karatu ba, da wata kila shi ma ya tsinci kansa a rikicin Makiyaya da Manoma da ke barazana ga harkokin tsaron Najeriyar. REUTERS/Dan Kitwood
Talla

Muhammadu Buhari wanda ke sanar da hakan yayin ziyarar aiki ta kwanaki biyu da ya kai jihar Bauchi da ke arewa maso gabashin Najeriyar ya kuma bukaci iyaye da su jajirce wajen ganin sun sanya yaransu a makarantu.

A cewarsa galibin rikice-rikicen na faruwa ne sanadiyyar rashin ilimi daga bangarorin biyu masu fada da juna.

Ziyarar shugaba Buharin zuwa Bauchi ita ce ta farko tun bayan hawansa mulki a shekarar 2015 inda ya kaddamar da wasu tarin ayyuka da suka kunshi asibiti, tituna da kuma wasu kayakin noma ga al'ummar jihar.

Kafin yanzu dai, Muhammadu Buhari a lokuta da dama ya shirya zuwa Bauchin amma yana soke tafiyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.