Fari da rikice rikice sun jefa sama da mutane miliyan 7 a cikin karancin abinci a Sahel
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:40
Kungiyar dake zura ido wajen daukar matakan riga kafi kan karamcin abinci a duniya OCDE, ta yi gargadin cewa, matsalar Fari da tashe tashen hankullan dake wakana sakamakon rikicin manoma da makiyaya ya jefa yankuna da dama na Sahel cikin matsalar karamcin abinci.Kungiyar ta OCDE dake da cibiyarta a birnin paris, ta ce yanzu haka kimanin mutane miliyan 7.1 ne ke bukatar agajin abinci a yankin na sahel, miliyan 3,7 daga cikinsu kuma, na a Arewacin tarayyar Najeriya ne.To ko ya ya kungiyoyin manoman Afrika ke kallon matsalar? Alhaji Mahamadu Magaji Gombe, sakataren yada labaran Kungiyar Manoma ta Najeriya ya yi mana tsokaci a tattaunawarsa da Mahaman Salisu Hamisu.