Isa ga babban shafi
Nijar

Nijar ta aike da shugabannin fararen hula gidan Yari

Akalla shugabannin manyan kungiyoyin fararen hula 4 ne yanzu haka ke garkame a gidan yarin Jamhuriyar Nijar bayan zanga-zangar karshen mako don kin jinin dokar haraji da gwamnatin ta haramta wadda ta juye zuwa rikici.

Wasu mambobin kungiyoyin fararen hula kenan lokacin da jami'an tsaro suka kai sumamen kama su a Ofishinsu da ke birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar.
Wasu mambobin kungiyoyin fararen hula kenan lokacin da jami'an tsaro suka kai sumamen kama su a Ofishinsu da ke birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar. Moussa Kaka/RFI
Talla

Shugabannin hudu na daga cikin mutane 23 da jami'an tsaro suka kame tun ranar Lahadi bayan da suka fito zanga-zanga duk da hanin da gwamnati ta yi.

Daga cikin shugabannin fararen hular da gwamnatin ta kame akwai wani jagoran adawa Nouhou Arzika sai masu fafutukar kare hakkin dan adam Moussa Tchangari da Ali Idrissa da kuma Lauya mai fafutukar kare hakkin dan adam Lirwana Abdourahamane.

Gwamnatin ta Nijar ta ce ta haramta zanga-zangar ta ranar Lahadi ne saboda an shiryata a kuraren lokaci, yayinda ta ce mutanen hudu ta na zarginsu da jagorantar lalata dukiyar al'umma da kuma karya dokar gwamnati.

Tun a jiya Litinin ne dai kungiyar kare hakkin dan adam ta Amnesty International ta bukaci sakin mutanen 23 cikin gaggawa, amma maimakon hakan zai gwamnatin ta iza keyar shugabannin hudu zuwa gidan yari.

Tuni dai gwamnatin ta Nijar ta yi umarnin kulle gidan talabijin da na Rediyo mallakin Ali Idrissa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.