Boko Haram ta saki wasu yan matan Dapchi
A yau talata,kungiyar Boko Haram ta saki wasu daliban makatarantar Dapchi,a baya dai gwamnatin Najeriya ta zabi ci gaba da tattaunawa a maimakon amfani da karfi domin kubutar da daliban Dapchi da sauran daliban Chibok da ke hannun Boko Haram.
Wallafawa ranar:
Kunna - 00:21
Rahotanni daga yankin na nuni da cewa biyar daga cikin daliban sun mutu a lokacin da yan boko haram ke kokarin ficewa da su daga Dapchi.
Indan aka yi tuni Shugaba Buhari ya ce, Najeriya na aiki cikin wata yarjejeniya da kungiyoyin kasashen ketare da masu sulhu don ganin an ceto ‘yan matan ba tare da cutar da su ba.
Shugaban ya kuma mika godiya ga Amurka bisa tallafinta na yaki da ta’addanci a Najeriya, yayin da kuma ya jinjina wa dakarun kasar da ya ce, suna bukatar karin samun horo da kayayyakin aiki.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu