Sarkozy na Faransa na tsare saboda wata badakalar rashawa
A cikin watan Agustan shekarar 2016 ne mai shigar da karar birnin Paris ya bayyana aniyar gurfanar da tsohon shugaban kasar Faransa Nicolas Sarkozy a gaban kotun, tare da wasu makarabansa da ake zargi da karbar kudade ba bisa ka’ida ba, a yakin neman zabensa na shekara ta 2007.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
A shekara ta 2017 wata kotu a Farnsa ta zargi Sarkozy da tsohuwar Jam’iyyarsa ta UMP da boye wasu kudaden yakin neman zaben shi da suka kai kudi euro miliyan 18.
Amma tsohon shugaban na Faransa ya musanta zargin inda ya ce ba ya da masaniya game da kashe kudaden da suka zarce adadin wadanda aka ware domin yakin neman zabensa.
Sarkozy dai ya sha kaye a zaben 2012 da aka gudanar wanda tsohon Shugaban kasar Francois Hollande ya lashe.
Yayinda wasu daga cikin ma`aikatan kamfanin Bymalion suka amsa cewa tabbas wannan badakala ta auku tsakaninsu da tsohuwarJam`iyyar UMP ta Sarkozy, wasu rahotanni da masu bincike suka samu na nuni cewa tabbas Sarkozy ya karbi milyan biyar na Euro daga tsohuwar gwamnatin Libya a karkashin marigayi Kanal Ghadafi da suka taimaka a yakin zaben shekarar 2007.
Mista Sarkozy shi ne tsohon shugaban Faransa na biyu da ya ke fuskantar shari`a tun daga shekara ta 1958.
Nicolas Sarkozy na tsare yanzu haka a Nanterre a kasar ta Faransa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu