Isa ga babban shafi
Somalia

Harin bam ya hallaka mutane 27 a Mogadishu

Harin wasu bama-bamai da aka dana a jikin motoci ya hallaka akalla mutane 27 tare da jikkata wasu 20 a Mogadishu, babban birnin kasar Somalia.

Wani farar hula da ya jikkata a harin bama-bamai da aka kai a birnin Mogadishu
Wani farar hula da ya jikkata a harin bama-bamai da aka kai a birnin Mogadishu Feisal Omar/Reuters
Talla

Harin wanda budewar wuta ya biyo bayansa, ya auku ne a gaf da fadar gwamnatin kasar ta Somalia.

Harin da kungiyar al-Shebaab ta dauki alhakin kai wa ya zo ne kwana guda bayan da gwamnatin kasar ta yi gargadin yiwuwar aukuwar harin ta’addanci a babban birnin kasar.

A watan Oktoban bara, wani harin bam da aka dana a babbar mota, ya hallaka mutane 512, wanda shi ne hari mafi muni da aka taba gani a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.