Isa ga babban shafi
Masar

Kotun Masar ta daure 'yan uwa Musulmi saboda bore

Wata Kotu a Masar ta yanke wa ‘yan kungiyar ‘yan uwa Musulmi 33 hukuncin dauri daga shekaru 7 zuwa rai-da-rai saboda tashin hankalin da aka yi a lokacin wata zanga zanga a shekarar 2014.

Zanga-zangar da aka gudanar a shekarar 2014 bayan kawar da Mohammed Morsi daga karagar mulki
Zanga-zangar da aka gudanar a shekarar 2014 bayan kawar da Mohammed Morsi daga karagar mulki REUTERS/Amr Abdallah Dalsh
Talla

Tashin hankalin ya biyo bayan juyin mulkin da soji suka yi wa shugaba Mohammed Morsi, bayan zanga zangar adawa da gwamnatinsa.

Bayanan kotun sun nuna cewar, an yanke wa mutane 17 hukuncin rai da rai, yayin da 16 kuma suka samu hukuncin da bai kai haka ba.

Daurin rai-da-rai a kasar Masar na dauke da hukuncin shekaru 25 ne.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.