Isa ga babban shafi
Afrika ta Kudu

ANC za ta fayyace makomar shugaba Zuma a yau

Shugaban Jam’iyyar ANC mai mulki a Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya amince cewar kawunan 'ya'yan jam’iyyar a rarrabe suke, yayin da jam’iyyar ke ci gaba da fafutukar kawar da shugaban kasar Jacob Zuma daga kujerarsa, in da za ta gudanar da wani zama a yau don fayyace makomarsa.

Al'ummar Afrika ta Kudu na fatan kawar da shugaba Jacob Zuma daga karagar mulki
Al'ummar Afrika ta Kudu na fatan kawar da shugaba Jacob Zuma daga karagar mulki MARCO LONGARI / AFP
Talla

Masharhanta kan lamurran siyasa na ganin cewa, akwai yiwuwar kwamitin gudanarwar jam’iyyar ya bukaci Zuma ya sauka daga kujerarsa.

Mr. Zuma mai shekaru 75 na fuskantar zarge-zargen cin hanci da rashawa bayan shafe tsawon shekaru 9 akan karagar mulki.

Ramaphosa ya shaida wa dandazon al’ummar kasar da suka halarci bikin cika shekaru 100 da haihuwar Nelson Mandela cewa, za su kawo karshen batun kwan-gaba-kwan-baya game da makomar Zuma a yau Litinin.

Ramaphosa ya ce, samun nasarar magance wannan matsalar na da matukar tasiri ga Afrika ta Kudu da ma jam’iyyar ANC, kuma ya yi alkawarin sanya manufar ‘yan kasar akan gaba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.