Isa ga babban shafi
South Sudan

'Yan Sudan ta Kudu sun yi wa Amurka bore

Daruruwan mutane ne suka gudanar da zanga-zanga a gaban ofishin jakadancin Amurka da na Majalisar Dinkin Duniya a birnin Juba domin bayyana bacin ransu kan matakin haramta wa Sudan ta Kudu sayen makamai.

Wasu daga cikin 'yan Sudan ta Kudu da ke gwagwarmayar kawo karshen yakin basasar kasar
Wasu daga cikin 'yan Sudan ta Kudu da ke gwagwarmayar kawo karshen yakin basasar kasar STEFANIE GLINSKI / AFP
Talla

Masu zanga-zangar sun mika takardar korafinsu ga jami’an Majalisar Dinkin Duniyar, yayin da wasu kuma suka kai musu hari, in da aka raunana wata 'yar jarida mai daukar hoto.

Kasar Amurka ta gabatar da kudirin hana sayar wa Sudan ta kudu makamai saboda yadda bangarorin da ke rikici a kasar suka gaza aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiyar da suka kulla.

Rikicin basasar kasar ya haddasa asarar rayukan dubban mutane, yayin da miliyoyi suka kaurace wa gidajensu, in da kuma wasu da dama suka tsindima cikin matsalar yunwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.