Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Dimokuradiyyar

Jami’an gwamnatin Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo na fuskantar takunkumai daga Amurka

Amurka ta sanar da takunkumai a kan wasu manyan jami’an gwamnatin Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo, sakamakon rawar da suke takawa a rikicin siyasar kasar.

Joseph Kabila,Shugaban Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo
Joseph Kabila,Shugaban Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo REUTERS/Kenny Katombe
Talla

Kafin nan, Faransa ta jima da sanya wa mutanen hudu takunkumai tare da kwace kadarorinsu a kasar.

Tun a baya gamayyar jam’iyyun adawa a Jamhuriyar Congo suka cimma matsaya, domin tilastawa shugaban kasar Joseph Kabila, sauka daga mukaminsa.

Yan adawar sun tattauna ne kan zaman dirshan da Kabila ke cigaba da yi a kujerar shugabancin kasar tun daga shekarar 2001.

Yan adawan sun bayyana cewa zaman kabila a kujerar shugabancin kasar ya haifar da koma bayan gaske a fanoni daban –daban,saukar sa ne mafuta ga wannan kasa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.