Taron kawo karshen rikicin Masar da Habasha
Yau ake saran shugabannin kasashen Masar da Habasha da Sudan za su gudanar da wani taro a Addis Ababa domin samo hanyar warware rikicin dake tsakanin kasashen su kan makomar kogin Nilu.
Wallafawa ranar:
Kasar Masar ta dogara ne kacokan da ruwan da take samu daga kogin, yayin da Habasha ke shirin tare ruwan domin gina madatsar da zata samar da wutar lantarki matakin da zai jefa Masar da Sudan cikin kunci.
A watan Disamba, shugaba Abdel Fatah al Sisi ya bukaci baiwa Bankin Duniya damar shiga tsakani domin warware matsalar bayan bangarorin dake rikicin sun kasa fahimtar juna.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu