Isa ga babban shafi

‘Najeriya ta mika shugabannin ‘yan aware Kamaru’

Gwamnatin Kasar Kamaru ta tabbatar da cewar Najeriya ta mika mata shugaban ‘Yan awaren kasar Sisuku Ayuk Tabe da ta tsare tun ranar 5 ga wannan watan.

'Yan sanda na aikin sintiri a yankin 'yan awaren Kamaru
'Yan sanda na aikin sintiri a yankin 'yan awaren Kamaru STR / AFP
Talla

Ministan sadarwa kuma kakakin gwamnati Issa Tchiroma Bakary ya ce yanzu haka Mista Tabe tare da wasu magoya bayansa 47 na tsare a hannun gwamnati.

Mista Tchiroma ya ce ”Kamaru da Najeriya abokan juna ne kuma dayansu bai yadda da duk wani matakin tada zaune tsaye ba.”

A farkon watan Janairu nan ne hukumomin Najeriya suka tsare shugaban ‘yan awaren da wasu magoya bayan sa 9 a Abuja.

Kungiyar Amnesty International ta bayyana damurta matuka a game da bukatar Kamaru wajen mika wadannan mutane, wadda ta ce ba za a yi musu adalci ba a shari’a.

Sisiku dai na bukatan yankin ‘arewa maso yammaci da kuma kudu maso yammacin kamaru masu Magana da harshen turancin Inglishi su bale daga kamaru, inda a ranar 1 ga watan Oktoba 2017, ya ayyana yankin a matsayin mai-cin gashin kanta da ya yi mata lakabi da Ambazoniya.

Kazalika tun daga wannan lokaci ake samun rikici da hare-hare ga takwarorinsu masu amfani da harshen Faransanci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.