Bakonmu a Yau
Dr Tukur AbdulKadir kan kalaman batanci da Donald Trump ya yi akan Afrika
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:08
Majalisar Dunkin Duniya da kungiyar Tarayar Afrika sun yi Allah wadai da kalaman batanci da aka ruwaito Shugaban Amurka Donald Trump ya furta game da kasashen Africa da kasar Haiti da El Salvador. Duk da cewa Donald Trump ya musanta furta kalaman, kasashe da dama suna ta yin Allah wadai da azarbabin na sa. Kasar Botswana ta gayyaci jakadan Amurka dake kasar don nuna masa rashin jin dadinta game da furucin. Garba Aliyu Zaria ya tattauna da Dr Tukur AbdulKadir na Jami’ar Jihar Kaduna da ke Najeriya.