Za a kwashe baƙin-haure 10,000 daga Libya zuwa Turai
Gwamnatin Italiya ta ce akwai yiwuwar a mayar da mutane kimanin dubu goma da ke maƙale a ƙasar Libya zuwa Turai a cikin shekara ta 2018.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Wannan dai wani mataki ne na magance matsalar tsarewa da kuma cin zarafin ƴan ƙasashen waje a ƙasar ta Libya.
Ministan cikin gida na ƙasar Italiya Marco Minniti ya ce baƙin za su shiga Turai ne a ƙarƙashin wani shiri na taimakon jin ƙai, ba tare da faɗawa cikin haɗari ba.
Hakan na zuwa ne bayan da a ranar Juma’a aka kwashe wasu daga cikin mutanen da suka maƙale a Libya ɗin zuwa birnin Roma na ƙasar ta Italiya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu