Isa ga babban shafi
Zimbabwe

Mnangagwa ya zabi Chiwenga a matsayin mataimakinsa

Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa, ya bayyana tsohon babban hafsan sojin kasar da ya jagoranci kawo karshen mulkin Robert Mugabe, Janar Constantino Chiwenga mai ritaya, a matsayin mataimakinsa.

Tsohon babban Hafsan sojin kasar Zimbabwe Costantino Chiwenga.
Tsohon babban Hafsan sojin kasar Zimbabwe Costantino Chiwenga. REUTERS/Philimon Bulawayo
Talla

Sakataren yada labaran Zimbabawen George Charamba, ya kuma sanar da zabar ministan tsaron kasar Kembo Mohadi a matsayin mataimakin Mnangagwa na biyu.

Sanarwar ta ce aikin dukkanin mataimakan shugaban kasar ya fara aiki ne nan take.

A makon da ya gabata ne Chiwenga yayi ritaya daga mukaminsa na babban hafsan sojin Zimbabwe, wata guda da ‘yan kwanaki, bayan jogarantar sojoji wajen karbe ragamar tafiyar da kasar a ranar 15 ga watan da ya gabata, kafin daga bisani Robert Mugabe ya yi murabus.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.