Macron ya fara ziyara a Jamhuriyyar Nijar
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya isa Jamhuriyyar Nijar a ziyarar da zai fara yau a kasar wadda ke da nufin karfafa gwiwar dakarun sojin Faransa fiye da dubu 4 da ke aikin yaki da ta'addanci a Nijar.
Wallafawa ranar:
Bayan saukar shugaban na Faransa Emmanuel Macron ya samu tarbar takwaransa shugaban Nijar Issoufu Muhammadu a filin jiragen sama na Yamai babban birnin kasar inda kuma kai tsaye ya nufi sansanin sojin Faransa da ke cikin filin jirgin saman.
Bayan ziyarar Macron a Gao da Ouagadougou da kuma Abidjan, ziyarar Macron ga Jamhuriyyar Nijar ya nuna yadda shugaban ke da fatan ganin kasashen yammacin Afrikan sun samu ci gaba tare da yakar ayyukan ta’addanci.
Ziyarar ta Macron za ta kaishi har zuwa ranar Kirsimeti inda zai gudanar da bukukuwan Kirsimetin tare da dakarun sojin Faransar da ke yaki da ta’addanci a Kasar.
Kafin wucewar shugaban na Faransa Emmanuel Macron zuwa sansanin sojin sai da su ka yi wata ganawa ta musamman mai tsayi tare da Issoufu Muhammad.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu