Bakonmu a Yau
Hashim Suleiman kan zaben jam'iyyar ANC mai mulkin Afrika ta Kudu
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:29
Bayan yakin neman zabe mai zafi da ya raba kan 'ya'yan Jam’iyyar ANC a Afirka ta Kudu, an zabi mataimakin shugaban kasa Cyril Ramaphosa a matsayin sabon shugaban Jam’iyyar ta ANC, kuma dan takarar zaben shugabancin kasar a shekarar 2019, wanda ya samu kuri’u 2,440 yayin da abokiyar takarar sa Nkosana Dlamini Zuma ta samu kuri’u 2,261. Dangane da wannan nasara da kuma makomar Jam’iyyar a zabe mai zuwa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hashim Muhammed Suleiman na Jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria.