Isa ga babban shafi
Najeriya

An bai wa mutanen da suka taimakawa EFCC ladarsu

Majiya daga ma’aikatar kudin Najeriya ta bayyana cewa an bai wa wadanda suka taimaka wa hukumar yaki da rashawa ta EFCC da bayanai domin gano makuddan kudade a wani gida da ke unguwar Ikoyi a Lagos kudin ladarsu da suka Naira milyan 421.

Mukaddashin shugaban hukumar EFCC Ibrahim Magu
Mukaddashin shugaban hukumar EFCC Ibrahim Magu
Talla

Tun bayan da Majalisar dattawan Najeriya ta bukaci hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasar EFCC, da ta gaggauta bayyana mamallakan makuden kudaden da yawansu ya kai Dala Miliyan 43, wanda aka gano a wani kasaitaccen gida da ke unguwar Ikoyi a jihar Legas.

Sai dai hukumar ta EFCC ta sake samame a gidan, in da a wannan karo ta binciki sassan tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi da kuma tsohon shugaban jam’iyyar PDP mai adawa, Alhaji Ahmad Adamu Mu’azu.

Wannan na zuwa ne bayan wasu jami’an leken asiri sun ce, akwai yiwuwar an boye wasu kudaden daban a sassan gidan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.