Isa ga babban shafi
Najeriya

Karancin man fetur na kara ta'azzara a Najeriya

Al’ummar Najeriya na ci gaba da fuskantar karancin man fetur a sassan kasar daban-daban, lamarin da ke ci gaba da haddasa cunkuson ababen hawa a gidajen sayar da man baya ga karuwar farashinsa sabanin yadda gwamnatin kasar ta sanya kan Naira 145 kowace lita guda.

Karancin man fetur da kuma tsadarsa na ci gaba da ta'azzara a Najeriya, kasar da ke takama da arzikin man fetur.
Karancin man fetur da kuma tsadarsa na ci gaba da ta'azzara a Najeriya, kasar da ke takama da arzikin man fetur. REUTERS/Mohamed Abd El Ghany
Talla

A makon daya gabata ne, Majalisar zartaswar Najeriyar ta bukaci kamfanin mai na kasar NNPC ya kawo karshen matsalar karancin man da al'ummar kasar ke fuskanta.

Kawo yanzu dai farashin man a wasu sassan kasar ya kai sama da Naira 180 yayinda kuma duk da hakan ake ci gaba da fuskantar karancinsa a kasar wadda ke takama da arzikin man fetur.

Ko a cikin makon nan Shugaban kasar Muhammadu Buhari ya ci gaba da fuskantar suka kan yadda ya gaza kawo karshen matsalar man a dai dai lokacin da bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara ke kara kusantowa.

Kusan za a iya cewa karanci da kuma tashin farshin man fetur ya zama ruwan dare a Najeriyar musamman a lokacin shagulgulan al'adu ko na addinai lamarin da wasu ke dora alhakin hakan kan manyan dillan man kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.