Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Congo

Jamhuriyar Congo: An fara sauraron shari'ar masu cin zarafin mata

Hukumomin kare hakkin dan adam a Jamhuriyar Demokradiyar Congo, sun sanar da fara sauraron karar mayakan 'yan tawayen da ke gabashin kasar 18, da ake zargi da cin zarafin kananan yara mata 46, ciki har da ‘yar watanni 18 da haihuwa.

Kungiyoyin kare hakkin dan adam sun dade suna zargin mayakan 'yan tawayen Jamhuriyar Congo, da yi wa mata fyade a gabashin kasar, a matsayin makamin yaki.
Kungiyoyin kare hakkin dan adam sun dade suna zargin mayakan 'yan tawayen Jamhuriyar Congo, da yi wa mata fyade a gabashin kasar, a matsayin makamin yaki. Reuters/Finbarr O'Reilly
Talla

An fara shari’ar ce, bayan dagewar da masu fafutukar kare hakkin dan adam suka yi, kan bukatar tilas a hukunta wadanda aka samu da laifi.

A na sa ran shari’ar, zata shafe makwanni ana gudanar da ita.

Kungiyoyin fararen hula na fatan a zartar da hukunci mai tsanani kan jami’an tsaron da ake zargin sun yi amfani da karfi wajen cin zarafin kananan yaran mata a matsayin makamin yaki.

A shekarun 2013 zuwa 2016 ne aka zargi wasu jami’an tsaro da cin zarafin kananan yara a wani kauye mai suna Kavumu a kasar ta Jamhuriyyar Dimukradiyyar Congo.

Masana sun yi hasashen cewa duk da matakan da kasar ke dauka a ‘yan shekarun nan kan jami’an tsaro, dangane da cin zarafi, ko kisan gilla, har yanzu al’amarin na kara kazanta, kasancewa a garuruwan da ke kan iyakar kasar a yankin gabashi, dukkanin bangarorin sojin gwamnati da 'yan tawaye suna yi wa mata fyade a matsayin makamin yaki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.