Isa ga babban shafi
Najeriya

Zanga-zangar adawa da korar malamai dubu 20 a Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta yi Allah wadai da zanga-zangar da kungiyar kwadago ta NLC ta shirya domin adawa da shirinta na korar malaman firamire sama da dubu 20.

Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufa'i
Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufa'i RFI-HAUSA
Talla

A jiya ne shugaban Kungiyar kwadagon Ayuba Waba ya jagoranci wannan zanga-zangar zuwa Majalisar dokokin jihar dan bayyana rashin amincewarsu da matakin korar malaman.

Ita dai gwamnatin jihar Kaduna, ta ce za a sallami malaman daga aiki ne saboda nuna gazawa lokacin da aka gabatar ma su da jarrabawa ‘yan aji hudu domin tantance kwarewarsu, inda sama da dubu 20 daga  cikin malamam suka fadi a jarrabawar.

To sai dai shugaban kwadagon sun bayyana jarrabawar a matsayin wadda aka shirya da nufin korar malaman ko ta halin kaka.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.