Isa ga babban shafi
Nijar

Kotu ta danka 'ya'yan Hama Amadou a hannun gidan marayu

Kotu a birnin Yamai na Jamhuiryar Nijar ta bayar  da umurnin kwace yara 16 daga cikin yara sama da 20 da aka bayyana cewa an sayo su ne daga kasashen ketare, inda kotun ta bayar da umurnin ci gaba da kula da su a wani gidan marayu da ke birnin Yamai.

Hama Amadou (a hagu) da Mahamadou Issoufou.
Hama Amadou (a hagu) da Mahamadou Issoufou. AFP/Issouf Sanogo/Farouk Batiche/Montage RFI
Talla

Daga cikin wadanda aka kwacen har da yara biyu wadanda tsohon shugaban majalisar dokokin kasar Hama Amadou ke ikirarin cewa ‘yayansa.

Yanzu haka da dama daga cikin iyayen wadannan yara na tsare a gidan yari, bayan da kotu ta same su da laifin cewa an sayo yaran ne daga Najeriya, yayin da daya daga cikin wadanda kotun ta sama da laifi a wannan batu tsohon shugaban majalisar dokokin kasar Hama Amadou ya gudu daga kasar kimanin shekaru biyu da suka gabata, duk da cewa matarsa wadda ta yi ikirarin cewa ita ta haifi yara ke tsare a gidan yari.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.