Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Congo

"Mutane miliyan 3 na fuskantar hadarin yunwa a Jamhuriyar Congo"

Shugaban hukumar bada agajin abinci ta majalisar dinkin duniya David Beasley ya bukaci manyan kasashen duniya da su kai taimako zuwa lardin Kasai na Jamhuriyar dimokaradiyyar Congo da tashin hankali ya dai-daita.

Tashin hankali ya jefa mutanen yankin Kasai na Jamhuriyar Congo, cikin hadarin fuskantar yunwa, bayan rasa rayukan sama da mutane 3,300 da kuma tilastawa sama da miliyan daya tserewa daga gidajensu.
Tashin hankali ya jefa mutanen yankin Kasai na Jamhuriyar Congo, cikin hadarin fuskantar yunwa, bayan rasa rayukan sama da mutane 3,300 da kuma tilastawa sama da miliyan daya tserewa daga gidajensu. AFP/File
Talla

Beasley ya ce sama da mutane miliyan uku ne a yankin na Kasai ke fuskantar hadarin fadawa yunwa, tare da gargadin cewa muddin ba’a dauki mataki ba, dubban daruruwan yara ka iya rasa rayukansu nan da watanni kalilan.

A watan Agustan shekara ta 2016 tashin hankali ya barke a yankin na Kasai bayan mutuwar wani basaraken gargajiya, lamarin da yayi sanadin mutuwar sama da mutane 3000 da kuma raba wasu miliyan 1 da rabi da gidajensu.

Tashin hankalin yayi kamari ne bayanda wasu mayaka mabiyan mai sarautar gargajiyar Kamuina Nsapu, suka kaddamar da harin ramuwar gayya kan sojin kasar da suka zarga da kashe shugaban nasu, wanda gwamnati taki amincewa da shugabancin yankin na Kasai da yake.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.