Isa ga babban shafi
Najeriya-tattalin arziki

Arzikin Najeriya zai bunkasa kasashen kudu da sahara-IMF

Hukumar bada lamuni ta duniya IMF ta yi hasashen cewa tattalin arzikin kasashen kudu da sahara zai bunkasa da kusan kashi uku da rabi sakamakon farfadowar tattalin arzikin Najeriya a fannin fetir da ayyukan noma.

Ginin kamfanin mai na NNPC a Najeriya
Ginin kamfanin mai na NNPC a Najeriya REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Hasashen rahoton na IMF ya ce, Najeriya za ta samu ci gaban tattalin arziki da kusan kashi 1 a bana, haka kuma zai kai kusan kashi biyu a badi.

Najeriya ta fuskanci tabarbarewar tattalin arziki sakamakon faduwar farashin mai, al’amarin da ya datse yawan kudaden da kasar ke samu.

A dayan bangaren kuma, rahoton na IMF ya ce, za a samu ci gaba a fannin mai a Angola, in da aka samu sauyin shugabanci bayan kawo karshen mulkin shekaru 38 na Eduardo dos Santos.

Amma hasashen ya nuna rashin tabbas a Afrika ta Kudu saboda rikicin siyasar jam’iyya mai mulki ta ANC.

Sannan rahoton ya yi gargadin cewa za a fuskanci karancin abinci da fari a kasashen Gambia da Sudan ta Kudu da kuma Somalia.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.