Isa ga babban shafi
Najeriya

Za a yi shari’ar wasu ‘Yan Boko Haram a asirce

Rahotanni a Najeriya sun ce za a yi shari’ar wasu da ake zargi ‘Yan kungiyar Boko Haram ne a asirce ba tare da ba ‘yan jarida damar halartar zaman kotun ba.

Wasu 'Yan boko Haram da suka mika wuya a Maiduguri
Wasu 'Yan boko Haram da suka mika wuya a Maiduguri RFIHAUSA/Bilyaminu
Talla

Wani Jami’ in Ma’aikatar Sharia a Najeriya ne ya shaidawa kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP cewa za a shariar ‘yan kungiyar Boko Haram 1,600.

Jami’in ya ce an tsayar da wannan shawara ne saboda matakan tsaro bayan wani tattaunawa tsakanin Jami’an Gwamnati da kuma jami’an tsaro na farin kaya.

A ranar 9 ga watan gobe ne ake sa ran fara shariar wadanda ake zargin ‘yan kungiyar Boko Haram ne da ke tsare a wuraren daban-daban.

Hukuncin kare hakkin dan adam sun dade suna sukar jami’an tsaron Najeriya da kame fararen hula da sunan ‘yan Boko Haram ba tare da an gabatar da su a kotu ba

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.