Isa ga babban shafi
Gabashin Afirka

'Yara sama da 800,000 ke fuskantar bala’in yunwa'

Kungiyar Agaji ta World Vision ta ce yanzu haka yara sama da 800,000 ke fuskantar bala’in yunwa a Gabashin Afirka sakamakon rashin abinci mai gina jiki da kuma tashe tashen-hankulan da ake samu.

Wasu daga cikin yaran 'yan gudun hijiran Somalia
Wasu daga cikin yaran 'yan gudun hijiran Somalia REUTERS/Thomas Mukoya
Talla

Hukumar kula da kananan yara ta Majalisar Dinkin Duniya, UNICEF, ta ce tashe-tashen hankulan da ake samu a kasashen Sudan ta kudu da Somalia da kuma tsananin farin da aka samu a Gabashin Afirka sun jefa rayuwar yara kanana miliyan 15 cikin hadari, saboda rashin abinci mai gina jiki da tsabtacacen ruwan sha da samun kula da lafiya da kuma ilimi.

Kungiyar World Vision ta ce kasashen Habasha da Somalia da kuma Kenya sun fuskanci matsalar yunwa tsakanin kananan yara a cikin makwannin da suka gabata, inda yankuna da dama suka ce sama da kashi daya bisa uku na yaran su na fama da rashin lafiya.

Daraktan kungiyar a Gabashin Afirka, Christopher Hoffman, ya ce suna cikin mawuyacin hali yanzu haka ganin yadda yara sama da 800,000 ke fama da tamowa.

Daraktan ya ce muddin ba’a dauki matakin gaggawa ba akasarin yaran na iya rasa rayukan su.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.