Isa ga babban shafi
Africa ta Kudu

Shugaba Jacob Zuma Ya Sake Fuskantar Matsalar Siyasa a Garin sa.

Wata Kotu a kasar Africa ta Kudu ta zartas da cewa zaben da aka yi wa wani bangare dake goyon bayan Shugaba Jacob Zuma a kauyen sa shekaru biyu da suka gabata, ya sabawa doka saboda haka an soke.

Shugaba Jacob Zuma na Africa ta Kudu.
Shugaba Jacob Zuma na Africa ta Kudu. rfi
Talla

Hukuncin Babban Kotun da aka zartas a Cape Town na nuna takun saka da ake samu cikin jam'iyar dake Mulki ANC, wanda zai iya dagula kokarin sa na ganin tsohuwar matarsa Nkosazana Dlamini-Zuma ta maye gulbinsa a matsayin shugaban kasa.

Yankin shugaba Jacob Zuma na KwaZulu Natal dake gabashin kasar na fama da rikici kuma yankin na da tasiri a wajen zabe a taron kasar na Babbar jam'iyar dake mulki ANC.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.