Isa ga babban shafi
Togo

Majalisar Togo za ta tattauna batun yi wa kundin tsarin mulki gyara

Majalisar dokokin kasar Togo za ta gudanar da zama na musamman a ranar talatar mai zuwa domin tattauna batun yi wa kundin tsarin mulkin kasar gyara domin sanya wasu daga cikin bukatun 'yan adawa da yanzu haka ke can suna gudanar da tarzoma.

Masu zanga-zanga a birnin Lomé, Togo, ranar 6 ga watan satumbar  2017.
Masu zanga-zanga a birnin Lomé, Togo, ranar 6 ga watan satumbar 2017. REUTERS/Noel Kokou Tadegnon
Talla

Bayanai sun ce majalisar na shirin amincewa da daftarin dokar da ke bayar da damar dawo da tsohon kundin tsarin mulkin kasar na shekarar 1992, wanda ke kayyade wa'adin shugabancin kasar sau biyu babu kari da kuma sauran bukatun 'yan adawar da suka share tsawon kwanaki suna gudanar da zanga-zanga a birnin Lome da sauran sassan kasar.

A jiya alhamis, manzon musamman na MDD a yammacin Afrika Mohammed Ibn Chambas ya kai ziyara a kasar, inda ya gana da wakilan 'yan adawa da kuma bangaren gwamnati domin kwantar da hankula.

Lamurran dai sun tsaya cik, da suka hada da na tattalin arziki, ma'aikatun gwamnati da masu zaman kansu musamman a birnin Lome da wasu manyan biranen kasar ta Togo.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.