Kamaru: Wasu dalibai sun kauracewa komawa karatu
Akasarin Daliban makarantun dake kudu maso yammacin Kamaru masu amfani da harshen Ingilishi sun kauracewa komawa makaranta sakamakon bukatar fitowa zanga zanga da shugabannin yankin suka yi, kan yadda ake musguna musu.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun ce an girke tarin ‘yan sanda cikin damara, domin kaucewa tada tarzoma a Buea, yayin da wakilin kamfanin dillancin labaran Faransa AFP, yace kashi daya bisa 5 ne kawai na daliban makarantun suka koma karatu.
A makon jiya shugaba Paul Biya ya bada umurnin sakin shugabanin matasan da suka shirya zanga zangar a shekarar bara, wadda ta haifar da tahsin hankali.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu