Amnesty ta shawarci Najeriya da Kamaru a kan Boko Haram
Kungiyar Amnesty International tace sabbin hare haren da kungiyar Boko Haram ta kaddamar, daga watan Afrilu na wannan shekara, sun yi sanadiyyar mutuwar fararen hula 381 a kasashen Kamaru da Najeriya, yayinda wasu miliyoyi ke bukatar agajin gaggawa.
Wallafawa ranar:
Amnesty tace alkaluman da ta tattara a Arewacin Kamaru da Jihohin Barno da Adamawa dake Najeriya na kunar bakin wake, na da tada hankali, ganin yadda kungiyar ke amfani da mata da kananan yara mata wajen kai hare-haren.
Yayin zantawar da yayi da sashin Hausa na RFI, Isa Sanusi, babban jami’in lura da sashin yada labaran kungiyar ta Amnesty International, ya ce kwai bukatar gwamnatocin Najeriya da Kamaru, su dauki matakan gaggawa domin kare fararen hula daga sabbin hare-haren.
Amnesty ta shawarci Najeriya da Kamaru a kan Boko Haram
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu