Harin gurneti ya raunata mutane a Burundi
Rundunar ‘yan Sandan kasar Burundi ta ce akalla mutane 29 sun jikkata, yayinda mutun daya ya rasa ransa a wani harin gurneti da aka kai cikin babban birnin kasar Bujumbura, a daren jiya Alhamis.
Wallafawa ranar:
Kakkakin ‘yan sandan kasar Pierre Nkrukiye, ya ce an kai harin ne kan wata mashaya da ke yankin Buyenzi a babban birnin, ya zuwa yanzu ba’a gano wanda yake da hannu wajen kai shi ba,
Tun a watan Afrilun shekara ta 2015, Burundi ta fada cikin rikicin siyasa, bayanda shugaban kasar Pierre Nkrunziza, ya sanar da aniyarsa ta sake neman shugabancin kasar, wa’adi na uku.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu