Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Dimokaradiyar Congo

Jamhuriyyar Congo: 'Yan adawa sun bai wa Kabila wa'adi

Gamayyar jam’iyyun adawa a Jamhuriyar Kongo sun cimma matsayar daukar wasu jerin matakai, domin tilastawa shugaban kasar Joseph Kabila, sauka daga mukaminsa.

Shugaban Jamhuriyyar Dimokaradiyyar Congo Joseph Kabila, a babban birnin kasar Kinshasa.
Shugaban Jamhuriyyar Dimokaradiyyar Congo Joseph Kabila, a babban birnin kasar Kinshasa. REUTERS/Kenny Katombe
Talla

Sanarwar ta zo ne bayan kammala taron kwanaki biyu tsakanin wakilan ‘yan adawar kasar a birnin Kinshasa, inda suka tattauna kan zaman dirshan da Kabila ke cigaba da yi a kujerar shugabancin kasar tun daga shekarar 2001.

Mai magana da yawun ‘yan adawar Francois Muamba, ya ce, a ranar 8 ga watan Agustan mai zuwa, zasu gudanar da yajin aikin gama gari na tsawon kwanaki 2, a mtsayin gargadi, yayinda kuma a ranar 20 ga watan ma Agusta za’a gudanar da zanga-zanga a birnin Kinshasa da sauran lardunan kasar 25.

Muamba ya kara da cewa idan har kabila ya cigaba da zama a kujerar shugabancin kasar, har zuwa karshen watan Satumba kuwa, to fa daga ranar 1 ga watan Oktoba zasu daina daukarsa a matsayin shalataccen shugaban kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.