Jamhuriyyar Congo: 'Yan adawa sun bai wa Kabila wa'adi
Gamayyar jam’iyyun adawa a Jamhuriyar Kongo sun cimma matsayar daukar wasu jerin matakai, domin tilastawa shugaban kasar Joseph Kabila, sauka daga mukaminsa.
Wallafawa ranar:
Sanarwar ta zo ne bayan kammala taron kwanaki biyu tsakanin wakilan ‘yan adawar kasar a birnin Kinshasa, inda suka tattauna kan zaman dirshan da Kabila ke cigaba da yi a kujerar shugabancin kasar tun daga shekarar 2001.
Mai magana da yawun ‘yan adawar Francois Muamba, ya ce, a ranar 8 ga watan Agustan mai zuwa, zasu gudanar da yajin aikin gama gari na tsawon kwanaki 2, a mtsayin gargadi, yayinda kuma a ranar 20 ga watan ma Agusta za’a gudanar da zanga-zanga a birnin Kinshasa da sauran lardunan kasar 25.
Muamba ya kara da cewa idan har kabila ya cigaba da zama a kujerar shugabancin kasar, har zuwa karshen watan Satumba kuwa, to fa daga ranar 1 ga watan Oktoba zasu daina daukarsa a matsayin shalataccen shugaban kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu