Isa ga babban shafi
DR Congo

Hukumomin Kasar Congo Sun Sanar Da Babu Cutar Ebola A Kasar

Kasar Jamhuriyar Democradiyya ta Congo yau Asabar ta sanar da cewa ta yi bankwana da sake bullar cutar Ebola tun daga yau, kasancewar kwanaki 42 ke nan cur ba’a ji labarin sake bullar cutar ba.

Wasu ma'aikatan lafiya a kasar DR Congo a lokacin da cutar ta sake barkewa
Wasu ma'aikatan lafiya a kasar DR Congo a lokacin da cutar ta sake barkewa congovoice.org
Talla

A kasar Congo inda aka fara samun cutar cikin shekara ta 1976,  aka sake samun bullar cutar kwanakin baya inda aka ce ta kashe mutane takwas.

Ministan Lafiya na kasar Oly Ilungu ya sanar cikin wata sanarwa cewa yanzu an tabbatar da cewa babu sauran cutar a fadin kasar.

Jimi'llan mutane dubu sha daya da dari uku suka mutu a lokacin da cutar ta barke sosai a yammacin Africa a shekara ta 2014.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.