Mali
An kashe Dakarun Majalisar Dinkin Duniya uku a arewacin Mali
An kashe dakarun MDD uku tare da raunata wasu akalla takwas a yankin Kidal da ke arewacin Mali a wannan juma’a.
Wallafawa ranar:
Talla
Sanarwar da rundunar ta Majalisar Dinkin Duniya MINUSMA ta fitar ta bayyana cewa an kai wa dakarun hari ne da makamai masu linzame a daidai lokacin da suke kan aikin tallafa wa dakarun Mali domin wanzar da zaman lafiya da tsaro a yankin.
Ana samun karuwar hare-hare akan dakarun na MDD da ma na kasar ta Mali a yankin Kidal da ke kallo a matsayin babbar cibiyar Azibinawa ‘yan tawaye da kuma sauran kungiyoyin da ke dauke da makamai a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu