Isa ga babban shafi
DR Congo

EU zata karawa Jami’an Congo takukumai

Kungiyar Kasashen Turai ta ce tana nazarin karawa manyan jami’an Gwamnatin Jamhuriyar Dimokuradiyar Congo Karin takunkumi saboda ci gaba da tashin hankalin da ake samu a kasar.

EU zata kara kakabawa jami'an gwamnatin Joseph Kabila takukumai
EU zata kara kakabawa jami'an gwamnatin Joseph Kabila takukumai REUTERS/Kenny Katombe
Talla

Wata majiyar diflomasiyar kungiyar ta ce mutane tara takunkumin zai shafa wajen rufe asusun ajiyar su na bankuna da hana tafiye tafiye, saboda yadda suke taimakawa rikicin.

Kafin wadannan akwai wasu 7 da aka sanyawa takunkumin a watan Disambar bara, cikin su harda hafsoshin soji da 'Yan Sanda.

Zaman lafiya ya gaggara samuwa a Congo tun lokacin da Shugaba Joseph Kabila ya bayyana bukatar tsawaita wa'adin mulkinsa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.