Sankarau ya kashe mutane 180 a Nijar
Wasu alkalumman Majalisar Dinkin Duniya sun ce kusan mutane 180 suka mutu sakamakon cutar Sankarau daga watan Fabrairun bana, yayin da kusan 3,000 suka kamu da cutar a sassan kasar.
Wallafawa ranar:
Rahoton na OCHA hukumar kula da ayyukan jin-kai ta Majalisar Dinkin Duniya ya ce tsakanin watan Janairu zuwa Mayu, kimanin mutane 3,037 suka kamu da cutar.
Rahoton kuma ya ce adadin mutane 179 Sankarau ya kashe a Nijar daga Janairu zuwa Mayu.
Cutar ta fi yin kamari a yankunan kudanci da yammacin Nijar, kuma rahoton ya ce har yanzu ana fama da Sankarau a yankin Maradi.
A bana cutar Sankarau ta kashe mutane sama da 1,000 a Najeriya yayin da mutane kusan 14,000 suka kamu da cutar musamman a arewacin kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu