Isa ga babban shafi
Nijar

Babu ribar da Nijar ta samu daga kamfanin Areva

Wasu kungiyoyi uku masu zaman kansu ONE, Oxfam da kuma Sherpa, sun ce ba wata ribar da gwamnatin Nijar ta sama a cinikin Uranium tsakaninta da kamfanin Areva a wani rahoton da suka fitar a jiya alhamis.

Kamfanin Areva na Faransa ke aikin hako arzikin Uranium a Nijar
Kamfanin Areva na Faransa ke aikin hako arzikin Uranium a Nijar AFP PHOTO / ISSOUF SANOGO
Talla

Kungiyoyin sun ce kudaden da Nijar ta karba ba su taka kara sun karya ba duk da cewa bangarorin biyu sun tattauna tare da sabunta yarjejeniyar da ke tsakaninsu ta wannan bangare.

Kungiyoyin sun kalubalanci kamfanin na Areva da kuma gwamnatin Nijar da su fito su bayyana wa duniya kudaden da ake samu a ciniki.

Rahoton ya ce a tsakanin shekara ta 2014 zuwa 2015, kudaden da Nijar ke samu daga Uranium sun ragu da kimanin Euro milyan 15 ba tare da wani dalili ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.