Isa ga babban shafi
Afrika ta Tsakiya

Amurka ta kakabawa wasu ‘Yan Seleka da Balaka takunkumi

Amurka ta sanya takunkumai a kan shugabannin wasu kungiyoyin ‘yan daba guda biyu a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya sakamakon rawar da suke takawa wajen tunzura jama’a da rikicin kasar mai nasaba da kabilanci da addini.

Rikicin Afrika ta tsakiya ta samo asali ne bayan mayakan Seleka sun hambayar da gwamnatin Francois Bozize
Rikicin Afrika ta tsakiya ta samo asali ne bayan mayakan Seleka sun hambayar da gwamnatin Francois Bozize AFP PHOTO / PACOME PABANDJI
Talla

Wadanda matakin ya shafa sun hada da Abdoulaye Hisseme tsohon shugaban Seleka, da kuma wani mai suna Maxime Mokom jigo na kungiyar Anti-Balaka.

Sannan takunkumin ya haramtawa Amurkawa da kamfanonin kasar yin hulda da mutanen inda aka kuma rufe asusun ajiyarsu a Amurka.

Rikicin Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya ya kashe daruruwan mutane tare da raba dubbai da gidajensu.

An zargi mutanen ne da kokarin yamutsa kuri’ar raba gardama kan kundin tsarin mulki da gudanar a 2015 tare da yin zagon kasa ga jagorancin shugaba Faustin-Archange.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.