Isa ga babban shafi
Nijar

Ba zan sauya kundin tsarin mulki ba-Issoufou

Shugaban Jamhuriyar Nijar Mahamadou Issoufou ya ce babu abinda zai sa shi sauya kundin tsarin mulkin kasar dan neman wa’adi na uku bayan karewar wa’adinsa a shekarar 2021.

Shugaban Jamhuriyar Nijar  Issoufou Mahamadou
Shugaban Jamhuriyar Nijar Issoufou Mahamadou
Talla

Yayin da yake amsa tambayoyi kan cikar sa shekara guda a karagar mulki, shugaban ya ce burin sa shirya karbaben zabe da duniya za ta amince da shi a shekarar 2021.

Shugaba Issofou ya ce shi cikkaken mai bin tafarkin demokradiya ne, saboda haka ba zai dauki kan sa a matsayin wanda babu wanda zai iya maye gurbin sa ba.

Idan ya samu nasarar kamala wa’adin sa, shugaban zai zama na farko a tarihin Nijar da zai mika mulki ga wani shugaban kasa ta hanyar zabe.
Elhj Dudu Rahama daga bangaren Adawa ya bayyana cewa sun sa ido a kai.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.