Ba zan sauya kundin tsarin mulki ba-Issoufou
Shugaban Jamhuriyar Nijar Mahamadou Issoufou ya ce babu abinda zai sa shi sauya kundin tsarin mulkin kasar dan neman wa’adi na uku bayan karewar wa’adinsa a shekarar 2021.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Kunna - 01:02
Yayin da yake amsa tambayoyi kan cikar sa shekara guda a karagar mulki, shugaban ya ce burin sa shirya karbaben zabe da duniya za ta amince da shi a shekarar 2021.
Shugaba Issofou ya ce shi cikkaken mai bin tafarkin demokradiya ne, saboda haka ba zai dauki kan sa a matsayin wanda babu wanda zai iya maye gurbin sa ba.
Idan ya samu nasarar kamala wa’adin sa, shugaban zai zama na farko a tarihin Nijar da zai mika mulki ga wani shugaban kasa ta hanyar zabe.
Elhj Dudu Rahama daga bangaren Adawa ya bayyana cewa sun sa ido a kai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu