Isa ga babban shafi
Sudan ta Kudu

An zargi sojin Sudan ta Kudu da kone gidaje sama da 3,000

Kungiyoyi masu zaman kansu da ke sa’ido kan yakin da ake fafatawa a kasar Sudan ta Kudu, sun ce sojin gwamnati sun kone dubban gidajen fararen hula a karshen shekara ta 2016 da ta gabata.

Wata karamar yarinya daga cikin dubban jama'ar Sudan ta Kudu da suka tsere zuwa sansanin 'yan gudun hijira na Bidi Bidi a kan iyakar kasar da arewacin Uganda.
Wata karamar yarinya daga cikin dubban jama'ar Sudan ta Kudu da suka tsere zuwa sansanin 'yan gudun hijira na Bidi Bidi a kan iyakar kasar da arewacin Uganda. REUTERS/James Akena/File Photo
Talla

Rahoton da masu fafutukar suka fitar, na daga cikin zargin cin zarafin dan ‘adam mafi karfi da ake kan sojin Sudan ta Kudu a cikin shekaru 3 da kasar ta shafe cikin yakin basasa.

Jami’an sa ido da suka kaiwa kauyuka 3 ziyara a yankin Yei da ke kudancin kasar, sun ce a kauye guda kadai, sojin kasar sun kone gidaje akalla dubu uku.

Sai dai gwamnatin kasar ta musanta zargin inda ta dora laifin kone gidajen da kuma sauran laifukan yaki na take hakkin dan'adam da ke aukuwa a kasar, kan mayakan ‘yan tawaye, sai kuma wutar daji da gwamnatin kasar ta ce ita ce silar konewar mafi yawancin gidajen fareren hular a kauyukan kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.