Isa ga babban shafi
Sudan ta Kudu

Sudan ta Kudu na siyan makamai a cikin yunwa

Wani rahoton sirri da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ya ce, gwamnatin Sudan ta Kudu na amfani da kudaden da ta samu a harkar man fetir wajen siyan makamai, a dai dai lokacin da kasar ke fama da matsalar yunwa.

Sudan ta Kudu na siyan makamai duk da matsalar yunwar da ta kefama da ita
Sudan ta Kudu na siyan makamai duk da matsalar yunwar da ta kefama da ita REUTERS/Jok Solomon
Talla

Rahoton wanda Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP ya samu , ya bukaci a dakatar da siyar wa Sudan ta Kudu da makamai, matakin da kasar Amurka ta amince da shi amma Kwamitin Sulhun na Majalisar Dinkin Duniya ya yi watsi da shi a kuri’ar da ya kada a cikin watan Disamban da ya gabata.

Gwamnatin Sudan ta Kudu dai na ci gaba da sanya hannu kan yarjejeniyar cinikayyar makamai duk da sanarwar da ke cewa, al’ummar kasar na mutuwa saaboda yunwa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.