'Yan bindiga sun kai wa 'yan agaji hari a Sudan ta Kudu
Wasu 'yan bindiga a Sudan ta kudu sun kai hari kan wata tawagar kungiyar agaji, in da suka kashe mutane biyu daga cikin tawagar yayin da kuma suka jikkata 3.
Wallafawa ranar:
Kungiyar kula da kaurar baki ta sanar cewar, 'yan bindigan sun kai harin ne kan tawagar da ke komawa daga garin Yirol, bayan sun ta yi musu kwanton-bauna, ta hanyar bude wuta.
Kungiyar ta ce ba ta iya gano maharan ba a kasar da ke ci gaba da fuskantar bala’in yunwa da yaki.
Ita ma kungiyar Medicins San Frotiers ta ce an kai hari a asibitin da take aiki a Wau Shilluk, in da aka kwashe magungunan da ke ciki.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu