Isa ga babban shafi
Nijar

'Yan adawa na zanga-zanga a Nijar

Gungun ‘yan adawa a Nijar sun fito suna zanga-zanga a yau a birnin Yamai ta kin jinin gwamnatin shugaba Mahamadou Issoufou tare da neman ganin an ba bangaren shari’a ‘yanci.

'Yan adawa sun mamaye harabar Majalisa a Yamai
'Yan adawa sun mamaye harabar Majalisa a Yamai
Talla

‘Yan adawar kuma na kukan tsadar rayuwa da matsalar cin hanci da rashawa da rashin tafiyar da gwamnati ta hanyar da ta dace.

Masu zanga-zangar dai sun mamaye harabar majalisa a Yamai suna yayata cewa “Tayi Tauri, ka fice ya isa haka nan”.

Bukatun masu zanga-zangar kuma sun hada da neman a saki fursunonin siyasa da aka cafke a shekarar 2015 kan zargin yunkurin juyin mulki, sannan sun bukaci ficewar dakarun Faransa da Amurka da Jamus da suka kafa sansanonin yakar ‘yan ta’adda a Mali da Libya.

Zanga-zangar dai ta yi karo da wadda aka taba gudanarwa a watan Janairu da ke nuna goyon baya ga jagorancin shugaba Mahamadou Issoufou.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.